‘
Yan Bindiga a garin Akaleku village dake karamar hukumar Obi ta jihar Nasarawa sun kashe wani Ango inda suka yi garkuwa da Amaryarsa.

Harin ya saka fargaba a tsakanin mutane sosai.
Maharan sun kai harinne ranar Laraba da misalin karfe 11 na dare.
Sun kashe Angon me suna Alu Anzaku wanda aka daurawa aure ranar 12 ga watan Afrilu.
Zuwa yanzu dai babu wata magana daga bakin jami’an tsaro game da lamarin.