Saturday, December 13
Shadow

Hukumar ‘yansanda ta saki sunayen mutane dubu 10 da suka yi nasara wajen neman aikin

Hukumar ‘yansanda ta PSC ta saki bayanan mutane dubu 10 da suka yi nasarar tsallakewa mataki na gaba a neman aikin dansandan.

Mutane 61,092 ne dai aka ajiye gefe wanda basu tsallake ba zuwa wannan matsayi.

Hukumar tace dan tabbatar da an yi adalci wajan fitar da sunayen ta yi aiki tare da majalisar tarayya, da hukumar tabbatar da an yi raba daidai wajan bada aikin gwamnati, da kuma hukumar ‘yansanda.

Tace ta tabbatar an baiwa kowace karamar hukuma a Najeriya cikin 774 da ake dasu damar wakilci a cikin wadanda aka dauka din.

Shugaban hukumar, Ikechukwu Ani ne ya bayyana hakan.

Karanta Wannan  Kalli Hoton matar da aka kama da harsasai 2000 zata kaiwa 'yan Bindiga a jihar Zamfara, da kuma wasu 'yan Boko Haram da suka tuba

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *