Monday, May 12
Shadow

IMF ta baiwa Gwamnatin Tinubu shawarar ta kara kaimi wajan karbar Haraji

Kungiyar bada Lamuni ta Duniya, IMF ta baiwa Gwamnatin tarayya shawarar cewa su kara kaimi wajan karbar haraji.

Wakiliyar kungiyar, Kristalina Georgieva ce ta bayyana haka a wata sanarwa da ta fitar a birnin Washington DC.

Ta bayyana cewa, ya kamata gwamnatin ta yi amfani da fasahar zamani wajan karbar harajin.

Ta bayyana cewa, bayar da shawara irin wannan ya zama dole musamman lura da cewa farashin man fetur da Najeriya ta dogara dashi wajan samun kudin shiga ya fadi a kasuwannin Duniya.

Karanta Wannan  Kalli bidiyon yanda Sheikh Pantami ya fashe da kuka saboda shaukin son Annabi(SAW) yayin da yake wa'azi, lamarin ya jawo cece-kuce

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *