Monday, March 17
Shadow

Jam’iyyar PDP ta lashe gaba dayan zaben kananan hukumomin da aka gudanar a jihar Osun

Rahotanni daga zaben kananan hukumomin jihar Osun da ya gabata ya nuna cewa, Jam’iyyar PDP ce ta lashe zaben a kafatanin kananan hukumomin jihar.

Kwamishinan zabe na jihar, Hashim Abioye ne ya bayyana hakan bayan kammala zaben inda yace PDP ce ta yi nasara a kananan hukumomi 30 da mazabu 323 dake fadin jihar.

Yace an samu nasarar kammala zaben cikin nasa.

Yace Jam’iyyu 18 ne suka yi takara a zaben kuma PDP ce ta lashe zaben na kananan hukumomi dana kansiloli baki daya.

Karanta Wannan  Hotuna:Kalli yanda Rahama Sadau ta kaiwa Halima Atete ziyara

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *