
Jihar Legas ta nemi masu haya da su kai karar duk wani me gida da ya nemi su biya kudin haya na shekara 2.
Jami’ar Hukumar kula da gidaje ta jihar, Barakat Bakare ce ta bayyana hakan a wata hira da aka yi da ita a gidan Talabijin TVC.
Tace gwamnan jihar na kokarin ganin mutane sun samu gidajen haya da sauki sannan kuma za’a saka ido da tabbatar da an bi doka wajan bayar da hayar.