Monday, April 14
Shadow

Kalli Bidiyo: Baban Dan Bello ya taba zuwa sata a Kabari, tun daga nan ne ya bar garinsu na Galadanci ba’a sake jin duriyarsa ba saboda Abin Kunya>>Inji Murtala Gamji, Shugaban dattawan Matasan Najeriya wanda ya fito kare Shaikh Bala Lau

Wani me suna Murtala Gamji, Shugaban dattawan Matasan Najeriya ya bayyana cewa ba zasu bari a rika taba malamai suna kyalewa ba.

Ya bayyana hakane a wata bidiyo da kafar ATP Hausa ta wallafa.

Ya kara da cewa, ko da fasto na garine aka ci zarafinsa ba zasu bari ya wulakanta ba zasu fito su kareshi.

Da yake jawabi da kuma ikirarin baiwa Sheikh Bala Lau Kariya, ya kara da cewa, Dan Bello bashi da asali me kyau.

Inda yace asalin mahaifinsa sata ya je yi a makabarta aka bishi, tun daga nan ne ya bar garinsu na Galadanci har yau bai dawo ba.

Karanta Wannan  'Yan Bindiga sun budewa motar matafiya wuta a hanyar Sokoto zuwa Minna, 2 sun Mùtù wasu sun jikkata

Kalli Bidiyon a kasa:

Me zaku ce?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *