
Bayan yaduwar Bidiyon wani zargin Luwadi da aka ce ana yo da yara a gidan yarin Goron Dutse dake Kano, Hukumar Hisbah ta aike da wakilanta gidan yarin.
Kuma bayan kammala bincike, sun ce wannan zargi da aka yi ba gaskiya bane.
Hukumar tace a kwanannan har saukar Qur’ani aka yi a gidan yarin hakanan wasu masu laifin da ake tsare dasu ma sun Samu Digiri da sauransu amma duk ba’a yada ba sai masha’a aka yada.
Hukumar ta yi kira ga mutane dasu daina yada abinda basu da tabbaci akansa.