
A kasar Morocco inda ake buga gasar AFCON, An ga fastar siyasa ta dan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu watau, Seyi Tinubu.
Dan Fafutuka, VDM ne ya ga fastar inda lamarin ya dauki hankula sosai bayan da aka ga wani Bidiyon yana cewa lallai dan shugaban kasar idonsa a rufe yake kan neman mukamin siyasa.
Da yawa dai suj ce hakan bai dace ba dan ba wajan siyasa bane.
Akwai dai rahotannin dake cewa, dan shugaban kasar na neman takarar gwamnan jihar Legas.