
Babban malamin Addinin Islama, Sheikh Kabir Gombe ya bayyana cewa masu zaginsu akan cewa basa wa’azi me zafi irin wanda suka yi zamanin Mulkin tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan basu da wuta basu da Aljannah.
Yace Shi Allahn da suke yi danshi ya sani.
Yace kuma ko a lokacin Goodluck Jonathan ba a farkon Mulkin sa suka fara mai wa’azi me zafi ba sai da aka yi wasu abubuwan da basu dace ba.
Ana dai ta zargin Malaman Cewa suna samu a jikin Gwamnati ne shiyasa basa iya fada mata gaskiya.