
‘Yar Najeriya dake zaune a kasar Ingila, Maryam Isha Olamide tace wani dan uwanta dan kudu ya tambayeta wai akwai Hausawa dake zaune a kasar Ingila?
Ta bashi Amsar cewa Eh, akwai.
Ta gaya masa cewa, tana da abokai maza da mata dake zaune a kasar Ingila.
Tace kawai su basu cika surutu bane, yawancinsu karatu ke kaisu, kuma idan sun gama suna komawa gida Najeriya dan basu dauki Ingilar Aljannar Duniya ba.