
Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta NDLEA ta kama kulli 20 na hodar iblis da aka boye a tsakanin litattafan addini da za’a yi safararta zuwa kasar Saudiyya.
Shugaban hukumar, Femi Babafemi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.
Yace an yi kamenne ranar 15 ga watan Afrilunnan da muke ciki, saidai bai bayar da karin haske kan ko an kama wadanda suka yi yunkurin aikata wannan laifi ba.