Sunday, December 14
Shadow

Kasar Canada zata fara koro ‘yan Najeriya gida

Rahotanni sun bayyana cewa, kasar Canada na shirin tsaurara matakai na daukar ‘yan kasashen waje aiki a kasar dake zuwa Cirani.

Hakan na nufin ‘yan kasashen waje da yawa dake aiki a kasar na fuskantar barazanar korarsu zuwa kasashen su, ciki hadda ‘yan Najeriya.

Kasar Canada din tace a yanzu kaso 10 cikin 100 ne kawai na ma’aikatan kamfanoni za’a rika barin ana daukar ‘yan kasashen waje inda sauran ‘yan asalin kasar Canada din za’a dauka.

Dan hakane dole a yanzu kamfanonin kasar zasu rage ma’aikatansu wanda ba ‘yan asalin kasar ba da maye ‘yan asalin kasar.

Karanta Wannan  Hukumomin sojin Amurka sun sace kudin da aka ware dan ciyar da sojojin kasar Abinci

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *