Tuesday, March 18
Shadow

Kiristancin Arewa, Maguzawa, da sauran mutanen Arewa ta tsakiya sunce basa tare da sauran mutanen Arewa dake cewa basa son Tinubu

Mutanen Arewa ta tsakiya da suka hada da Kiristoci da Maguzawa, da mutanen jihar Jos da sauransu sun bayyana cewa, basa tare da sauran mutanen Arewa dake cewa basa son Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.

Sun bayyana cewa su a shekarar 2027, Shugaba Bola Ahmad Tinubu ne zabinsu.

Saidai wadannan mutane dake son ballewa dan nuna goyon bayan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, kalilan ne daga cikin mutanen Arewa.

Saidai a gefe daya kuma, Mafi yawan ‘yan Arewa sun bayyana cewa basa tare da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu inda suka ce ba zasu zabeshi ba a zaben 2027.

Kungiyoyin fafutuka da yawa daga Arewa sun bayyana cewa ba zasu goyi bayan sake zaben shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a shekarar 2027 ba.

Karanta Wannan  Ji abinda Bello Turji yawa mutanen Moriki a jihar Zamfara da ya tayar da hankula

Shugaban kungiyar hadaka ta kungiyoyin Arewar, Jamilu Charanchi ya bayyana cewa matukar wahalar rayuwa da matsin tattalin arziki ya ci gaba a Najeriya, ‘yan Arewa ba zasu zabi Bola Ahmad Tinubu a shekarar 2027 ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *