Friday, December 5
Shadow

Ko da ‘yan Arewa basu yi Tinubu ba zai ci zaben 2027, saboda duka kudanci shi zasu zaba, kuri’a kadan yake nema daga Arewa ya ci zabe>>Inji Ayodele Fayose

Tsohon Gwamnan jihar Ekiti, Ayodele Fayose ya bayyana cewa kudancin Najeriya gaba daya na Shugaba Tinubu ne.

Yace Tinubu kuri’u kadan yake bukata daga Arewa ya ci zabe.

Fayose ya bayyana hakanne a hirar da aka yi dashi a gidan talabijin na Channels TV.

Yace Peter Obi ne zai zo na 2 sannan sai jam’iyyar ADC zata zo na 3 sai watakila PDP ta zo na 4.

Ya bayyana cewa idan aka lura da Tarihin da Tinubu ya kafa a siyasar Najeriya, da wuya ya fadi zaben 2027.

Karanta Wannan  Hotuna: An Hangi Wani Malami Da Takobi, Ya Yin Gabatar Da Huɗubar Juma'a.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *