Tuesday, March 17
Shadow

Kungiyar malaman kwalejojin Kimiyya da fasaha, ASUP sun baiwa Gwamnatin Tarayya wa’adin akwanaki 21 a biya musu bukatunsu ko su tafi yajin aiki

Kungiyar malaman Kwalejojin Ilimin Kimiyya da Fasaha ASUP ta baiwa gwamnatin tarayya wa’adin kwanaki 21 a biya musu bukatunsu ko su tafi yajin aiki.

Shugaban kungiyar, Comrade Shammah Kpanja ya bayyana hakan ga manema labarai a Abuja ranar Juma’a.

Yace daya daga cikin abubuwan da suke bukata shine a kafa hukuma me kula da ayyukan kwalejojin Ilimin kimiyya da fasaha.

Sannan kuma ya kara da cewa auna neman a daidaita sakamakon kammaga kwalejojin ilimin kimiyya na HND da Kwalin Digiri da ake bayarwa bayan kammala Jami’o’i.

Karanta Wannan  Dan majalisar dokoki na majalisar jihar Nasarawa, Musa Gude ya dauki hankula saboda nada masu taimaka masa guda 106

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *