Thursday, February 26
Shadow

Likitoci dubu 30 ake dasu a Najeriya

shugaban kungiyar Likitoci ta Najeriya, Professor Bala Audu ya bayyana cewa, Likitoci dubu 30 ne ake dasu a Najeriya.

Ya bayyana hakane a wajan wani taron kungiyar likitocin da ya wakana a Jihar Katsina.

Yace a shekaru 5 da suka gabata, Likitoci dubu 15 ne suka bar Najeriya zuwa kasashen Waje.

Yace kowane Likita daya yana ganin marasa Lafiya dubu 8. Wanda a ka’ida marasa lafiya dari shida ne ya kamata ace kowane likita na gani.

Karanta Wannan  Za'a gyara titunan zuwa dakin dafa abinci na shugaban kasa Tinubu, da wanda jiragen samansa ke bi da wanda ake bi dan kai masa ziyara akan Naira Biliyan 9.8

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *