Wednesday, May 28
Shadow

Likitoci dubu 30 ake dasu a Najeriya

shugaban kungiyar Likitoci ta Najeriya, Professor Bala Audu ya bayyana cewa, Likitoci dubu 30 ne ake dasu a Najeriya.

Ya bayyana hakane a wajan wani taron kungiyar likitocin da ya wakana a Jihar Katsina.

Yace a shekaru 5 da suka gabata, Likitoci dubu 15 ne suka bar Najeriya zuwa kasashen Waje.

Yace kowane Likita daya yana ganin marasa Lafiya dubu 8. Wanda a ka’ida marasa lafiya dari shida ne ya kamata ace kowane likita na gani.

Karanta Wannan  Manyan Limaman Kiristoci sun yi ruwan Allah wadai ga gwamnatin Tinubu inda suka ce Ya magance matsalar Talauci data tsaro

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *