Friday, December 5
Shadow

Maganar Wike ya baiwa ‘ya’yansa manyan filaye a Abuja: Atiku ne saboda kiyayya yake son batamin suna>>Inji Wike

{“remix_data”:[],”remix_entry_point”:”challenges”,”source_tags”:[],”origin”:”unknown”,”total_draw_time”:0,”total_draw_actions”:0,”layers_used”:0,”brushes_used”:0,”photos_added”:0,”total_editor_actions”:{},”tools_used”:{},”is_sticker”:false,”edited_since_last_sticker_save”:false,”containsFTESticker”:false}

Ministan babban birnin tarayya, Abuja Nyesom Wike ya zargi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben shekarar 2023, Alhaji Atiku Abubakar da kala masa sharri.

Yace Atiku ne yasa ake shirin bata masa suna da maganar cewa wai ‘ya’yansa sun mallaki filaye da yawa a Abuja.

Wike ya bayyana hakane ta bakin kakakinsa, Lere Olayinka inda yace ‘ya’yansa kamar kowane dan Najeriya suna da ‘yancin mallakar filaye a ko ina suke so a fadin Najeriya.

Yace amma babu gaskiya a rahoton dake cewa, Ya baiwa ‘ya’yan Nasa filaye masu yawa a Abuja.

Wike ya kara da cewa, kamfanin Jordan Farms and Estates Limited kamfanine wanda ba mallakar ‘ya’yansa ba, wanda shine kamfanin da ake ta cece-kuce akan cewa an bashi filaye.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon sabuwar wakar habaici da aka ce Rarara yawa Ganduje bayan sauka daga shugabancin APC

Ya kara da cewa, masu binciken kuma idan suna da hujjar cewa kamfanin na ‘ya’yansa ne su fito su fada.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *