Sunday, June 28
Shadow

Maganar Wike ya baiwa ‘ya’yansa manyan filaye a Abuja: Atiku ne saboda kiyayya yake son batamin suna>>Inji Wike

{“remix_data”:[],”remix_entry_point”:”challenges”,”source_tags”:[],”origin”:”unknown”,”total_draw_time”:0,”total_draw_actions”:0,”layers_used”:0,”brushes_used”:0,”photos_added”:0,”total_editor_actions”:{},”tools_used”:{},”is_sticker”:false,”edited_since_last_sticker_save”:false,”containsFTESticker”:false}

Ministan babban birnin tarayya, Abuja Nyesom Wike ya zargi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben shekarar 2023, Alhaji Atiku Abubakar da kala masa sharri.

Yace Atiku ne yasa ake shirin bata masa suna da maganar cewa wai ‘ya’yansa sun mallaki filaye da yawa a Abuja.

Wike ya bayyana hakane ta bakin kakakinsa, Lere Olayinka inda yace ‘ya’yansa kamar kowane dan Najeriya suna da ‘yancin mallakar filaye a ko ina suke so a fadin Najeriya.

Yace amma babu gaskiya a rahoton dake cewa, Ya baiwa ‘ya’yan Nasa filaye masu yawa a Abuja.

Wike ya kara da cewa, kamfanin Jordan Farms and Estates Limited kamfanine wanda ba mallakar ‘ya’yansa ba, wanda shine kamfanin da ake ta cece-kuce akan cewa an bashi filaye.

Karanta Wannan  Game da hatsarin da Jarumi Adam A. Zango ya yi, bayanai na nuna an samu wasu marasa Imani sun sace masa wayar sa da kuɗin sa har da ɗan cincin ɗin da mahaifiyar sa tayi masa guzuri da shi da sauran abubuwan amfani

Ya kara da cewa, masu binciken kuma idan suna da hujjar cewa kamfanin na ‘ya’yansa ne su fito su fada.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *