Sunday, May 25
Shadow

Masu ikirarin Jìhàdì sun kàshè sojojin Najeriya hudu a sabbin hare-haren da suka kai Borno

Mayaƙan IS sun ƙara kai wa sojojin Najeriya hari, karo na biyu a cikin kwanaki biyu.

Rundunar sojin Najeriya ta ce maharan sun kashe dakarunta huɗu a wani sansanin su da ke kusa da garin Rann da ke kan iyakar ƙasar da Kamaru a ihar Borno.

A ranar Litinin ma IS ta kai hari a wani sansanin soji da ke yammacin Borno, a garin Marte, inda aka bayar da rahoton kisan sojojin Najeriya da dama.

Masu sharhi sun ce a baya bayan nan mayaƙan masu iƙirarin jihadi sun canza salon kai hare-hare, ciki harda amfani da jirgin sama marar matuƙi.

Karanta Wannan  YANZU-YANZU: A'in Ja'afaru Ta Zama Jakadiyar Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi ll

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *