Thursday, February 5
Shadow

Masu ikirarin Jìhàdì sun kàshè sojojin Najeriya hudu a sabbin hare-haren da suka kai Borno

Mayaƙan IS sun ƙara kai wa sojojin Najeriya hari, karo na biyu a cikin kwanaki biyu.

Rundunar sojin Najeriya ta ce maharan sun kashe dakarunta huɗu a wani sansanin su da ke kusa da garin Rann da ke kan iyakar ƙasar da Kamaru a ihar Borno.

A ranar Litinin ma IS ta kai hari a wani sansanin soji da ke yammacin Borno, a garin Marte, inda aka bayar da rahoton kisan sojojin Najeriya da dama.

Masu sharhi sun ce a baya bayan nan mayaƙan masu iƙirarin jihadi sun canza salon kai hare-hare, ciki harda amfani da jirgin sama marar matuƙi.

Karanta Wannan  Bayan da majalisa ta kwace mata motarta ta aiki, Kalli Motar Alfarma da Sanata Natasha Akpoti ta siya take tuka abinta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *