Tuesday, May 13
Shadow

Matasan da suka goyi bayan Buhari na kiran tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya fito takara a 2027

Shugaban tsohuwar kungiyar goyon bayan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, Dr. Jibril Mustapha, ya yi kiran tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya fito takarar shugaban kasa a shekarar 2027.

A sanarwar da ya fitar a Legas, yace ya kamata tsohon shugaban kasar ya amsa kiraye-kirayen da ake masa domin shine Najeriya ke bukata a yanzu.

Yace Najeriya a yanzu tana bukatar shugaban kasa wanda zai hada kan kasar kuma Tsohon shugaba Goodluck Jonathan na da wannan abun da ake bukata.

Karanta Wannan  Wata Sabuwa, an shigar da karar neman tsige shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu daga kan kujerarsa saboda cin zalin 'yan kasa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *