Wednesday, April 29
Shadow

Matasan da suka goyi bayan Buhari na kiran tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya fito takara a 2027

Shugaban tsohuwar kungiyar goyon bayan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, Dr. Jibril Mustapha, ya yi kiran tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya fito takarar shugaban kasa a shekarar 2027.

A sanarwar da ya fitar a Legas, yace ya kamata tsohon shugaban kasar ya amsa kiraye-kirayen da ake masa domin shine Najeriya ke bukata a yanzu.

Yace Najeriya a yanzu tana bukatar shugaban kasa wanda zai hada kan kasar kuma Tsohon shugaba Goodluck Jonathan na da wannan abun da ake bukata.

Karanta Wannan  An yi Allah wadai da wadannan matan saboda yanda suke kiran sauran mata da su je su bayar da kansu maza su basu kudi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *