Thursday, December 25
Shadow

Mu na fama da matsanancin ƙarancin ma’aikata – NAFDAC

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta ƙasa, NAFDAC, ta koka kan matsanancin ƙarancin ma’aikata.

Da ta ke ganawa da manema labarai a Legas a jiya Alhamis, shugabar hukumar, Farfesa Mojisola Adeyeye ta baiyana cewa a yanzu haka hukumar na da ma’aikata dubu 2 kacal a fadin ƙasar, inda ta ce hakan adadi ne mai matuƙar kankanta duba da irin aikin hukumar.

Ta yi kira da a ninka adadin ma’aikatan hukumar sau biyu ko sau uku, inda ta ce aikin da su ke yi na kare lafiyar al’ummar ƙasa baki daya na buƙatar wadatuwar ma’aikata don a samu sakamako mai kyau.

Karanta Wannan  Duk da Hukumar Hisbah ta Kano tace ta je gidan yarin Goron Dutse ta ga ba gaskiya a zargin Luwadi da ake da yara, Saidai da yawa sun ce basu yadda da binciken na Hisbah ba, ciki kuwa hadda tsohon hadimin shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *