Friday, May 30
Shadow

Muma dai Muna goyon bayan a baiwa ‘yan Najeriya damar rike Bìndìgà dan su kare kansu tunda dai jami’an tsaro sun gaza>>Sowore da Solomon Dalung

{“remix_data”:[],”remix_entry_point”:”challenges”,”source_tags”:[],”origin”:”unknown”,”total_draw_time”:0,”total_draw_actions”:0,”layers_used”:0,”brushes_used”:0,”photos_added”:0,”total_editor_actions”:{},”tools_used”:{},”is_sticker”:false,”edited_since_last_sticker_save”:false,”containsFTESticker”:false}

Tsohon ministan matasa da wasanni, Solomon Dalung da Dan takarar shugaban kasa kuma mawallafin jaridar Sahara Reporters, Omoyele Sowore sun nemi a baiwa ‘yan Najeriya damar rike Bindiga dan su kare kansu.

Sunce idan aka yi hakan za’a daina kashe-kashen da ake yi a jihohin Benue da Filato da sauransu.

Sun bayyana hakanne a wata ganawa da suka yi da manema labarai a Abuja.

Hakan na zuwane watanni 5 bayan da Sanata Ned Nwoko ya kai kudirin neman a baiwa mutane damar rike makamai dan kare kansu.

Shima lauya dan fafutuka, Deji Adeyanju yace idan dai jami’an tsaro ba zasu iya ba, ya kamata a baiwa mutane damar sayen bindiga dan kare kansu.

Karanta Wannan  Gwammatin Tinubu tace zata gina makamin kare dangi, watau Nokiliya, Saidai Minista yace kul kada a fara

Sowore yace mutane sun daina yadda da kariyar da jami’an tsaro ke ikirrin basu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *