Monday, April 6
Shadow

Mùtùwàr ‘yan Kwallon Kano, da Mùtùwàr mutane a Ambaliyar ruwan Jihar Naija, Kunki dakar mataki, kun bari mutane na ta mùtùwà>>Atiku Abubakar ya caccaki Gwamnatin Tinubu

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya caccaki gwamnatin tarayya inda yace basu dauki matakan da ya kamata ba gashi mutane na ta mutuwa.

Ya bayyana hakane a sakon ta’aziyya ga iyalan ‘yan kwallon Kano 22 da suka rasu a hadarin Mota. Inda yace ba iyalansu kadaine suka yi asararsu ba, hadda ma Najeriya baki daya.

Ya kuma bayyana Alhinin rasuwar mutane sama da 100 a ambaliyar ruwan garin Mokwa dake jihar Naira inda yace abin takaici ne.

Atiku ya baiwa Gwamnatin tarayya shawarar ta dauki matakan kula da titinan Najeriya dan rage ko kawar da yawaitr hadurra.

Sannan ya nemi da a dauki matakan hana ambaliyar ruwa musamman yanzu da ake fuskantar yawaitar ruwan sama.

Karanta Wannan  Ji yanda wani yayi barazabar kulle asusun ajiyarsa da bankin Ja'iz saboda bankin basu tura masa sakon taya Maulidi ba, yace abin takaici shine sauran bankunan da bana Musulunci ba sun tura masa sakon taya murnar Maulidi amma banda Ja'iz

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *