Saturday, December 13
Shadow

Mùtùwàr ‘yan Kwallon Kano, da Mùtùwàr mutane a Ambaliyar ruwan Jihar Naija, Kunki dakar mataki, kun bari mutane na ta mùtùwà>>Atiku Abubakar ya caccaki Gwamnatin Tinubu

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya caccaki gwamnatin tarayya inda yace basu dauki matakan da ya kamata ba gashi mutane na ta mutuwa.

Ya bayyana hakane a sakon ta’aziyya ga iyalan ‘yan kwallon Kano 22 da suka rasu a hadarin Mota. Inda yace ba iyalansu kadaine suka yi asararsu ba, hadda ma Najeriya baki daya.

Ya kuma bayyana Alhinin rasuwar mutane sama da 100 a ambaliyar ruwan garin Mokwa dake jihar Naira inda yace abin takaici ne.

Atiku ya baiwa Gwamnatin tarayya shawarar ta dauki matakan kula da titinan Najeriya dan rage ko kawar da yawaitr hadurra.

Sannan ya nemi da a dauki matakan hana ambaliyar ruwa musamman yanzu da ake fuskantar yawaitar ruwan sama.

Karanta Wannan  Da Duminsa: Kalli Bidiyon yanda Jirgin sojojin Najeriya yayi sukar Dole dauke da sojoji 11 a kasar Burkina Faso

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *