Friday, December 26
Shadow

Najeriya ta zo ta biyu a yawan mutane matalauta a Duniya

Tsohon shugaban Hukumar kididdiga ta kasa, NBS, Yemi Kale ya bayyana cewa, Najeriya ce ta biyu bayan India da ta fi kowace lasa yawan matalauta.

Yace akwai matalauta Miliyan 89 a Najeriya wanda hakan yana nufin kaso 40 na ‘yan Najeriya matalauta ne.

Ya bayyana hakane a cikin sakoshi na ranar ‘yanci.

Yace babban abinda ke kawo Talauci shine yanda gwamnati bata yin tsare-tsare masu kyau.

Karanta Wannan  Lakurawa sun kashe ƴan sanda biyu, sun yi awon gaba da shanu sama da 500 a Kebbi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *