Wednesday, December 17
Shadow
Buhari ya koma Najeriya bayan gabatar da shaida a kotun Paris

Buhari ya koma Najeriya bayan gabatar da shaida a kotun Paris

Duk Labarai
Tsohon shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari ya koma kasar bayan gurfana a gaban wata kotu a birnin Paris na kasar Faransa. Cikin wani bidiyo da tsohon mataimakinsa na musamman kan harkokin sadarwa, Bashir Ahmad ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya nuna lokacin da tsohon shugaban kasar ke sauka daga jirgi a jihar Katsina. A farkon makon nan ne tsoffin shugabannin Najeriya biyu, Olusegun Obasanjo da Muhammadu Buhari suka bayyana a gaban wata kotun cinikayya ta ƙasa da ƙasa da ke birnin Paris na a ƙasar Faransa domin ba da bahasi dangane da kwangilar aikin gina cibiyar samar da wutar lantarki ta Mambilla da ke jihar Taraba. Wani kamfani mai suna Sunrise Power ne dai ya kai gwamnatin Najeriya ƙara kan saɓa ƙa'idojin kwangilar, inda yake neman gwamnatin ta biya shi dalar Amurka biliyan...
Tsaffin Janarorin soja ne ke satar ma’adanai a Najeriya>>Oshiomhole

Tsaffin Janarorin soja ne ke satar ma’adanai a Najeriya>>Oshiomhole

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan jihar Edo, Adams Oshiomhole ya yi zargin cewa, tsaffin janarorin soja ne ke satar ma'adanai a Najeriya. Oshiomhole ya bayyana hakane a yayin da shugaban kwamitin dake kula da harkar hakar ma'adanai a majalisar,Sampson Ekong ke muka sakamakon binciken kwamitinsa ga majalisar. Oshiomhole wanda shine shugaban kwamitin dake kula da harkokin cikin gida ya bayyana cewa, sun san wadannan tsaffin janarorin dan kuwa koda a lokacin mulkin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari sai da ya rubuta mai wasika akan ayyukan nasu. Ya kara da cewa, wadannan masu hakar ma'adanai ba bisa ka'ida ba suna safarar muhgan makamai dan gudanar da ayyukansu kamar yanda ake yi a sudan ta kudu. Oshiomhole ya bayar da shawarar cewa, maganin wannan matsala shine a samar da rundunar jami'an tsar...
Bello Turji Ya Ce A Shirye Yake Ya Mika wuya – CDS

Bello Turji Ya Ce A Shirye Yake Ya Mika wuya – CDS

Duk Labarai
Duk da rahotannin da Turji ya bayar na mika wuya, babban hafsan tsaron ya ci gaba da cewa duk wanda ya aikata kisan kiyashi ba dole ba ne a tsira. Babban hafsan hafsoshin tsaron Najeriya Janar Christopher Musa a ranar Juma’a ya bayyana cewa fitaccen Jagoran ‘yan ta’adda Bello Turji ya bayyana cewa a shirye yake ya mika wuya. Yayin da yake shugabanta na biyu da kuma wasu hafsoshin sojin kasar kwanan nan da sojoji suka kama, babban hafsan hafsoshin tsaron kasar ya ce an tilastawa Turji watsi da mafi yawan wadanda ke karkashinsa, wanda hakan ke nuna a shirye ya ke ya ajiye makamansa. “Su (’yan ta’adda) suna cikin al’umma; mutane sun san su. Don haka, wani lokacin idan sun gan su, kafin ka sami bayanin, kamar sa'o'i biyu ne - mutumin ya motsa. Don haka, lokacin da bayanin ya isa gare ...
Hukumar EFCC na tsaka mai wuya inda aka samu jami’anta da sace kudade da kadarorin da aka kwato daga ma’aikatan Gwamnati

Hukumar EFCC na tsaka mai wuya inda aka samu jami’anta da sace kudade da kadarorin da aka kwato daga ma’aikatan Gwamnati

Duk Labarai
Hukumar yaki da rashawa da cin hanci ta EFCC na fama da matsalar jami'anta da ake kamawa da satar kudade da kadarori da aka kwato daga hannun jami'an gwamnati da masu rashawa da cin hanci. Wasu daga cikin jami'an hukumar an koresu daga aiki inda wasu kuma aka dakatar dasu dan yin bincike kan zargin satar kayan da aka basu kula wa dasu. Koda a shekarar data gabata, mutane 27 ne aka kora daga EFCC saboda satar kudaden da aka basu ajiya Hakanan kakakin EFCC a ranar 6 ga watan Janairu 2025 ya tabbatar da cewa suna binciken batan dala $400,000 da ake zargin wani jami'in hukumar ya sace. Hakanan akwai jami'an hukumar 10 da aka dakatar a reshenta na jihar Lagos inda ake zarginsu da satar Gwal da darajarsa ya kai na Naira Biliyan 1, da kudade dala $350,000 zuwa $400,00 wanda duka suka...
Kaso 77 na matan Najeriya na Amfani da man kara hasken fata>>Inji WHO

Kaso 77 na matan Najeriya na Amfani da man kara hasken fata>>Inji WHO

Duk Labarai
Kungiyar Lafiya ta Duniya, WHO ta bayyana cewa, kaso 77 cikin 100 na matan Najeriya na amfani da man kara hasken fata wanda ake cewa Bleaching. Hakan bmna zuwane yayin da wani rahoto yace ba matan ba kadai yanzu hadda kananan yara a Najeriya ana shafa musu man kara hasken fata. Rahoton na WHO yace mayukan kara hasken fata ne mafiya ci gaba da aka fi sayarwa a tsakanin mayukan shafawa a Duniya baki daya. Hakan na faruwa ne duk da irin illar da irin wadannan mayukan shafawar ke dauke da ita wanda ya hada da ragewa fata karfi da garkuwar da take dashi da kuma kara hadarin kamuwa da cutar daji.
Ana zargin DPO da yin lalata da karamar yarinya me shekaru 15 da aka tsare a fishin ‘yansanda a Katsina

Ana zargin DPO da yin lalata da karamar yarinya me shekaru 15 da aka tsare a fishin ‘yansanda a Katsina

Duk Labarai
Ana zargin DPO din 'yansanda dake Dutsinma, CSP Bello Gusau da yiwa karamar yarinya lalata wadda ake tsare da ita a ofishin 'yansanda. Wata kungiyar kare hakkin bil'adama HRTI ce shigewa yarinyar gaba inda suke nema mata hakkinta. Shugaban kungiyar Kwamared Maiyasin ya bayyana cewa sai da suka yi bincike suka tabbatar da cewa DPO din ya dauki yarinyar ya je ya kwana da ita a gidansa, ba'a ofishin 'yansanda ta kwana ba kamin su dauki mataki. Kwamishinan 'yansandan jihar Katsina, CP Aliyu Musa ya bayyana cewa an dakatar da DPO din inda aka fara bincike kan lamarin.
Ba zamu iya ci gaba da biyan tallafin wutar Lantarki ba>>Gwamnatin Tarayya

Ba zamu iya ci gaba da biyan tallafin wutar Lantarki ba>>Gwamnatin Tarayya

Duk Labarai
Shugaban kwamitin dake kula da yanda Gwamnatin tarayya ke kashe kudi, James Faleke ya bayyana cewa, Gwamnatin tarayya ba zata iya ci gaba da biyan kudij tallafin wutar lantarki ba. Ya bayyana hakane yayin da ma'aikatar kudi ke bayanin yanda zata kashe kudadenta a shekarar 2025. Gwamnatin tarayya dai ta ware Naira biliyan 705 dan biyawa 'yan Najeriya tallafin wutar a shekarar 2025. Saidai Falake yace sam babu bukatar hakan musamman lura da yanda farashin wutar labtarkin ke ta kara tashi kullun da kuma yanda darajar Naira ke ci gaba da faduwa.
An kama wannan tsagerar da ta sha Alwashin zin lalata da maza 100 a rana daya

An kama wannan tsagerar da ta sha Alwashin zin lalata da maza 100 a rana daya

Duk Labarai
Hukumomi a kasar Turkiyya sun kama wata tsagera data yi suna wajan nuna tsiraici me suna Ezra Vandan 'yar shekaru 23 saboda Alwashin da ta sha na yin lalata da maza 100 a cikin awanni 24. 'Yansanda a birnin Istanbul sun kama matar ne bisa zargin cewa abinda take da niyyar aikatawa ya sabawa al'adar kasar kuma zai jawo gurbacewar tarbiyya. Matar dai ta yi aniyar daukar bidiyon lalatar da zata yi kai tsaye tare da nunawa Duniya. Hakan na zuwane kwanaki kadan bayan da wata tsagerar me suna Brit Bonnie Blue ta yi ikirarin yin lalata da maza guda 1000 a rana daya.
Bamu yadda da karin kudin kiran waya ba, muna kiran ‘yan Najeriya su kauracewa kamfanonin sadarwa>>NLC

Bamu yadda da karin kudin kiran waya ba, muna kiran ‘yan Najeriya su kauracewa kamfanonin sadarwa>>NLC

Duk Labarai
Kungiyar Kwadago NLC ta bayyana cewa, bata yadda da karin kudin kiran waya na kamfanonin sadarwa ba da aka yi zuwa kaso 50 cikin 100. Shugaban kungiyar ta NLC, Joe Ajaero ne ya bayyana haka ranar Laraba ga manema labarai inda yace hakan ya zo ne a lokacin da ake fama da tsadar rayuwa gashi kuma babu kudin sayen kayan masarufi. Joe Ajaero yace amfani da kafafen sadarwa ya zamarwa 'yan Najeriya dole ta yanda suke kashe akalla kaso 10 cikin 100 na kudin shigarsu akan harkar sadarwa. Joe Ajaero yace kungiyar kwadago ta yi Allah wadai da wannan lamari inda yace basu amince dashi ba.