Monday, April 6
Shadow
Gwammatin Tinubu tace zata gina makamin kare dangi, watau Nokiliya, Saidai Minista yace kul kada a fara

Gwammatin Tinubu tace zata gina makamin kare dangi, watau Nokiliya, Saidai Minista yace kul kada a fara

Duk Labarai
Ministan wutar Lantarkin Najeriya, Adebayo Adelabu ya gargadi yunkurin hukumar makamashin Najeriya na samar da tashoshin makamin Nokiliya dan samar da wutar lantarki. Hukumar dai tace tana son yin hakanne dan samar da wutar Lantarki me karfin 1,200 Megawatt da zata magance matsalat wutar Lantarkin Najeriya. Shugaban Hukumar Makamashin, Anthony Ekedewa ya kaiwa ministan wutar lantarkin ziyara a ofishinsa a Abuja ranar Talata ind ya bayyana cewa suna shirin samar da tashoshin makamin kare dangi guda 4 a Najeriya. Yace idan suka yi nasara hakan zai samar da ingantacciyar wutar Lantarki me karfi sosai a Najeriya Yace suna son kafa wadannan tashoshin wutar ne a jihohin Kogi da Akwa-Ibom. Saidai yace basu da kudi amma suna neman hada kai da ma'aikatar wutar Lantarkin. Mini...
Budurwa ta yi karyar An yi garkuwa da ita, ashe dakin saurayinta ta tafi suka buga soyayya

Budurwa ta yi karyar An yi garkuwa da ita, ashe dakin saurayinta ta tafi suka buga soyayya

Duk Labarai
Wata daliba dake ajin karshe na jam'ar Jihar Ekiti, EKSU me suna Helen Kayode ta yi karyar an yi garkuwa da ita amma ashe dakin saurayinta ta tafi suka sha soyayya. Ta aikawa kanwarta da sakon cewa, ta shiga motar da ba ta gane mata ba inda daga baya tace an kaita wani kango ana tsare da ita. Sakon nata ya watsu sosai a kafafen sada zumunta sannan hankalin mutanen Iworoko-Ekiti da Ado-Ekiti ya tashi sosai inda daga canne ta fito. Kakakin 'yansandan jihar, SP Sunday Abutu ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace sun kama dalibar. Kuma ta amsa laifin data aikata na aika sakon garkuwa da ita amma na karya. Hukumar 'yansandan sun yi gargadin cewa kada a sake samun wanda yayi hakan in ba haka ba mutum zai fuskanci hukunci
Tabbas na bayar umarnin a ciro min kàn Wike sannan a kàshè Tinubu inda har nasa  ladar Naira Miliyan 100 ga wanda yayi hakan>>Nnamdi Kanu

Tabbas na bayar umarnin a ciro min kàn Wike sannan a kàshè Tinubu inda har nasa ladar Naira Miliyan 100 ga wanda yayi hakan>>Nnamdi Kanu

Duk Labarai
Shugaban haramtacciyar kungiyar IPOB dake son lafa kasar Biafra, Nnamdi Kanu ya aminta cewa ya sa a kashe masa ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ta hanyar ciro kansa. Sannan kuma yasa a kashe shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da kona kadarorinsa, inda har ya saka ladar Naira Miliyan 100 ga duk wanda yayi hakan. Wani shaida ne ya bayyana hakan a kotu inda yace Kani ya fadi hakanne a gidan Rediyon da ya bude. An kuma saurari maganar da Kanu yayi wadda aka nada a cikin Kotun inda aka jishi ana cewa, a kashe Wike saboda bai cancanci rayiwa ba sannan a kashe Tinubu a kona kadarorinsa sannan a kashe jami'an tsaro.
‘Yan gida daya su 5 sun mùtù bayan cin Abinci me guba

‘Yan gida daya su 5 sun mùtù bayan cin Abinci me guba

Duk Labarai
Wasu 'yan gida daya su 5 sun mutu bayan cin abinci me guba a garin Ogidi, dake karamar hukumar Idemili North ta jihar Anambra. Mahaifiyar su ma na can kwance rai hannun Allah a Asibiti. Lamarin ya faru ranar Asabar 3 ga watan Mayu 2025 kuma ya jefa mutanen garin cikin damuwa. Mahaifin yaran Pa Robinson Aghalu dan shekaru 76 wanda tsohon soja ne yace yaran nasa sun fara amai da ciwon ciki ne bayan cin abincin da mahaifiyarsu ta dafa. Su 6 ne suka ci abincin kuma guda 5 sun mutu. Kakakin 'yansandan jihar, SP Tochukwu Ikenga ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace sun dauki abincin dan zuwa a yi gwaji.
Ji Dalilin da yasa Hukumar EFCC suka naɗe Gudaji Kazaure zuwa Abuja

Ji Dalilin da yasa Hukumar EFCC suka naɗe Gudaji Kazaure zuwa Abuja

Duk Labarai
Hukumar EFCC a jihar Kano ta kama tsohon ɗan majalisar tarayya Hon. Muhammad Gudaji Kazaure bayan ta gayyaceshi ofishinta kuma ya kai kansa amma daga bisani ta naɗeshi zuwa Abuja. Bayanan da Zuma Times Hausa ta samu sun ce, EFCCin tana neman bayanan wasu kyaututtukan kudade naira miliyan 14 da suka shiga asusun bankin tsohon dan majalisar a wani lokaci a shekarar 2019. Me zaku ce?
Dalibar Da Ta Kammala Digiri Da Sakamako Mafi Daraja A Jami’ar Northwest Dake Kano Ta Koma Tallar Wainar Fulawa Bayan Rashin Samun Aikin Yi

Dalibar Da Ta Kammala Digiri Da Sakamako Mafi Daraja A Jami’ar Northwest Dake Kano Ta Koma Tallar Wainar Fulawa Bayan Rashin Samun Aikin Yi

Duk Labarai
Dalibar Da Ta Kammala Digiri Da Sakamako Mafi Daraja A Jami'ar Northwest Dake Kano Ta Koma Tallar Wainar Fulawa Bayan Rashin Samun Aikin Yi. A yayin jin ta bakin Kwamared Habiba Usman Garkuwa, wadda har ta taba zama shugabar dalibai na jami'ar da ta yi, ta ce ta raba takardun neman aiki adadin da ba za ta iya tunawa ba, amma har yanzu shiru don haka ta yanke shawarar fara soya wainar fulawa da awara. Habiba dai ta fita da sakamako mafi daraja Jami'ar Northwest a shekarar 2024 a fannin ilimin kimiyyar Biology, kamar yadda wanda ya fitar da rahoton, Abdulwahab Said Ahmad ya wallafa a Shafinsa na Facebook.
An kama Barawo bayan da ya saci Keke Napep a masallaci a jihar Naija

An kama Barawo bayan da ya saci Keke Napep a masallaci a jihar Naija

Duk Labarai
Hukumar 'yansandan jihar Naija sun yi nasarar kama wani barawon Keke Napep a jihar. Kakakin 'yansandan jihar, SP Wasiu Abiodun ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace lamarin ya farune ranar 5 ga watan April. Sunan Barawon da aka kama Abdulaziz Salisu kuma yayi satar ne yayin sallar Asuba a Dakwa. Yace bayan ya saci Keke Napep din yayi yunkirin kaiwa wani me suna Abubakar Mohammed dan ya sayar masa dashi. Yace ana tsaka da sallah ne Abdulaziz ya fita ya sace Keke Napep din amma sai 'yansanda suka kamashi a gadar Maje inda ya amsa cewa satota yayi.
Likitoci dubu 30 ake dasu a Najeriya

Likitoci dubu 30 ake dasu a Najeriya

Duk Labarai
shugaban kungiyar Likitoci ta Najeriya, Professor Bala Audu ya bayyana cewa, Likitoci dubu 30 ne ake dasu a Najeriya. Ya bayyana hakane a wajan wani taron kungiyar likitocin da ya wakana a Jihar Katsina. Yace a shekaru 5 da suka gabata, Likitoci dubu 15 ne suka bar Najeriya zuwa kasashen Waje. Yace kowane Likita daya yana ganin marasa Lafiya dubu 8. Wanda a ka'ida marasa lafiya dari shida ne ya kamata ace kowane likita na gani.