Friday, December 26
Shadow

Sanata Abubakar Sadiq Yar’adua ya fice daga jam’iyyar APC zuwa ADC

Sanata Abubakar Sadiq Yar’adua wanda ya wakilci mazabar Katsina ta tsakiya a majalisar tarayya ya bayyana cewa, ya fice daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar ADC.

A takardar da ya aikewa da mazabarsa ranar 28 ga watan Yuli, Tsohon Dan majalisar ya bayyana cewa, tsare-tsaren jam’iyyar APC sun jefa al’umma cikin halin kaka nika yi.

Yace da gaskene kalaman Malam Nasir El-Rufa’i da yace gwamnatin Tinubu ta koma ‘yan Bindigar birni.

Abubakar Sadiq ‘Yar’Adua wanda yayi takarar gwamnan jihar Katsina a zaben 2023 yace Gwamnatin Tinubu na biyewa Turawa ne wanda burinsu tara Duniya yana jefa ‘yan Najeriya a wahala.

Yace yana fatan shi da mabiyansa zasu koma jam’iyyar ADC nan gaba kadan

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon: Anata cece-kuce saboda ganin Dan shugaban kasa, Seyi Tinubu jami'an gwamnati sun tsaya a gefen jirgi suna gaisheshi, kamar dai yanda akewa shugaban kasa da Gwamnoni

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *