Friday, January 16
Shadow

Shugaba Tinubu ya bayar da umarnin sake rage farashin kayan abinci

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sake bayar da umarnin a sake rage farashin kayan abinci.

Shugaban ya bayar da wannan umarnin ne ga majalisar zartaswa, kamar yanda karamin Ministan noma, Senator Aliyu Sabi Abdullahi ya bayyanawa manema labarai a Abuja.

Ministan da yake magana ranar Laraba ya ce shugaban kasar yace a samar da yanda za’a rika safarar kayan abincin a Najeriya ta hanyar sauki ta yanda farashinsa zai sake sauka.

Hakan na zuwane a yayin da wasu manoma ke kukan cewa faduwar farashin kayan abinci na sa su tafka Asara.

Karanta Wannan  Ya kamata a rage zagin da ake min a rika godemin domin gaba dayan kudaden da aka samu daga cire tallafin Man fetur na rabar dasu ga 'yan Najeriya>>Shugaba Tinubu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *