Friday, July 17
Shadow

Shugaba Tinubu ya bayar da umarnin sake rage farashin kayan abinci

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sake bayar da umarnin a sake rage farashin kayan abinci.

Shugaban ya bayar da wannan umarnin ne ga majalisar zartaswa, kamar yanda karamin Ministan noma, Senator Aliyu Sabi Abdullahi ya bayyanawa manema labarai a Abuja.

Ministan da yake magana ranar Laraba ya ce shugaban kasar yace a samar da yanda za’a rika safarar kayan abincin a Najeriya ta hanyar sauki ta yanda farashinsa zai sake sauka.

Hakan na zuwane a yayin da wasu manoma ke kukan cewa faduwar farashin kayan abinci na sa su tafka Asara.

Karanta Wannan  Tsohon Hadimin Shugaban kasa, Bashir Ahmad yayi kira ga shugaba Tinubu da ya kawo Cristiano Ronaldo da sauran 'yan kwallon kasar Portugal Najeriya dan ya farantawa 'yan Najeriya rai kamin zaben 2027

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *