
Rahotanni sun bayyana cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya yafewa Kamfanin mai na kasa, NNPCL bashin dala Biliyan $1.42 da Naira Tiriliyan 5.57 da ya kamata NNPCL din su biya a asusun Gwamnatin tarayya.
Hakan na kunshene a cikin bayanan da hukumar kula da man fetur ta kasa, Nigerian Upstream Petroleum Regulatory Commission suka futar.
Rahoton yace fadar shugaban kasa ta bayar da umarnin yafe bashin da kuma gogeshi daga cikin takardun da aka rubutashi.