Tuesday, April 14
Shadow

Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya ce har yanzu yaki Amsa k9 daya daga cikin Tambayoyin da ICPC suke masa

Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, har yanzu bai amsa tambaya ko daya ba cikin Tambayoyin da ICPC suke masa.

Malam Nasiru Ahmad El-Rufai dai ya shafe kusan sama da sati biyu kenan a hannun ICPC tun da suka karbeshi daga hannun EFCC.

Ya bayyana cewa, dalilin da yasa ya ki amsa tambayoyin nasu shine binciken da ake masa na da alaka sa diyasa.

A baya dai ICPC ta kai samame gidan Malam Nasiru Ahmad El-Rufai inda tace ta gano abubuwa da yawa ciki hadda wata na’ura ta yiwa waya kutse.

A baya dai malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya yi ikirarin yiwa wayar me baiwa shugaban kasa shawara kan harkar tsaro, Malam Nuhu Ribadu kutse.

Karanta Wannan  Jihar Legas ta hana Masu gidajen haya karbar kudin haya na shekaru 2

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *