Wednesday, February 25
Shadow

Sojoji Sun Kàshè Manyan masu ikirarin Jìhàdì A jihar Bòrnò

{“remix_data”:[],”remix_entry_point”:”challenges”,”source_tags”:[],”origin”:”unknown”,”total_draw_time”:0,”total_draw_actions”:0,”layers_used”:0,”brushes_used”:0,”photos_added”:0,”total_editor_actions”:{},”tools_used”:{},”is_sticker”:false,”edited_since_last_sticker_save”:false,”containsFTESticker”:false}

A ranar Litinin, 9 ga watan Yuni 2025, dakarun haɗin gwiwa na sojoji sun kai farmaki maɓoyar ƴan ta’adda na Boko Haram da ISWAP a Nzalgana da ke ƙaramar hukumar Gujba da kuma yankin Timbuktu Triangle.

Sanarwar da rundunar ta fitar a shafinta na X ta ce an kashe ƴan ta’adda da dama ciki har da jagororinsu.

Daga cikin waɗanda aka kashe akwai Ameer Malam Jidda, wani babban kwamanda da ke da tasiri a ƙauyukan Ngorgore da Malumti.

Sojojin sun ƙara cewa sun kuma ƙwato makamai da wasu abubuwa masu muhimmanci a wani farmaki daban da suka kai Malamfatori.

A ‘yan kwanakin nan, hare-haren Boko Haram da ISWAP sun ƙaru, inda a watan da ya gabata ƙungiyar ta kai hari da jirgi mara matuƙi a garin Marte da ke Jihar Borno.

Karanta Wannan  Ba gaskiya bane, Ban sha komai ba, Matukin jirgin saman Air Peace ya karyata binciken da yace ya sha miyagun Qayoyi da Giyya a lokacin da yake tuka mutane 103

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *