Sunday, March 16
Shadow

Tafiye-Tafiyen da Tinubu yayi sun kawowa Najeriya zuba jari na dala Biliyan $50

Gwamnatin tarayya tace tafiye-Tafiyen da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ke yi sun kawowa Najeriya zuba jarin dala Biliyan $50.

Ministar masana’antu, Jumoke Oduwole ce ta bayyana hakan a wata ganawa da aka yi da ita ranar Talata a Abuja.

Tace shugaban ya halarci taruka irin su na manyan kasashe mafiya karfin tattalin arzikin a Duniya watau G20 wanda kuma kamfanoni da yawa suka hadu a wajan.

Tace wakilan wadannan kamfanoni da masu zuba jari sun kawo ziyara Najeriya kuma sun ga damar zuba jari kuma sun bayar da tabbacin zasu zo su zuba wannan jari a Najeriya.

Karanta Wannan  Bam ya kashe mutum biyu a wata Islamiyya a Abuja

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *