Friday, December 5
Shadow

Tinubu ya miƙa ta’aziyya kan rasuwar ƴan wasan Kano da su ka yi haɗari

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya nuna alhini da jimami da alhini bisa rashe-rashen da suka faru a jihohin Kano da Neja, yana mai bayyana lamarin a matsayin babban rashi ga ƙasa baki ɗaya.

A wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Juma’a, Shugaba Tinubu ya nuna matuƙar kaɗuwa kan hatsarin mota da ya rutsa da ‘yan wasan Jihar Kano a hanyarsu ta dawowa daga gasar wasanni ta ƙasa da aka kammala a Jihar Ogun.

Shugaban Ƙasa ya yi addu’ar Allah ya jikan waɗanda suka rasa rayukansu a cikin hatsarin, ya kuma roƙi Allah ya bai wa iyalansu da daukacin al’ummar Kano haƙuri da juriya.

Karanta Wannan  Hoto:Wannan mutumin ya mutu a dakin Otal bayan yin lalata da karuwa

Ya ce hanya mafi inganci ta girmama su ita ce ɗaukar matakan kariya domin rage aukuwar irin wannan ibtila’i a gaba.

Baya ga haka, Tinubu ya bayyana alhini kan ambaliya mai tsanani da ta afku a ƙaramar hukumar Mokwa da ke Jihar Neja, wacce ta yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama tare da raba daruruwan iyalai da muhallansu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *