Friday, December 5
Shadow

Tsare-tsaren Gwamnatin Tinubu ya jefa Mutanen Najeriya cikin matsanancin Talauci>>Inji Janar Buratai

Tsohon shugaban sojojin Najeriya, Janar Tukur Yusuf Buratai ya bayyana cewa, Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta jefa ‘yan Najeriya cikin matsin talauci.

Ya bayyana hakane a wajan taron zagayowar ranar haihuwar tsohon Ministan sufuri, Rotimi Amaechi.

Yace gwamnatocin baya a hankali suka rika jefa ‘yan Najeriya cikin talauci amma Gwamnatin Tinubu, Lokaci guda ta jefa mutane saboda tsare-tsaren ta data gudanar masu tsauri.

Saidai yayi fatan nan da shekaru biyu masu zuwa a samu saukin rayuwa wanda yace idan ba haka ba, akwai matsala.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: Na yi mamaki da naji ance Kwankwaso zai dawo APC, saboda a baya ya Zhaghi shugaba Tinubu sannan yace masu shiga APC Mahaukata ne>>Inji Ganduje

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *