Saturday, December 13
Shadow

Tsare-tsaren Gwamnatin Tinubu ya jefa Mutanen Najeriya cikin matsanancin Talauci>>Inji Janar Buratai

Tsohon shugaban sojojin Najeriya, Janar Tukur Yusuf Buratai ya bayyana cewa, Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta jefa ‘yan Najeriya cikin matsin talauci.

Ya bayyana hakane a wajan taron zagayowar ranar haihuwar tsohon Ministan sufuri, Rotimi Amaechi.

Yace gwamnatocin baya a hankali suka rika jefa ‘yan Najeriya cikin talauci amma Gwamnatin Tinubu, Lokaci guda ta jefa mutane saboda tsare-tsaren ta data gudanar masu tsauri.

Saidai yayi fatan nan da shekaru biyu masu zuwa a samu saukin rayuwa wanda yace idan ba haka ba, akwai matsala.

Karanta Wannan  Tura sojoji kasar Benin Republic da shugaba Tinubu yayi babban laifine da ya kamata ace an tsigeshi daga shugabancin Najeriya>>Inji Lauya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *