
Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Dr. Dalhatu Bafarawa yace ‘yan siyasar yanzu basu da kishin kasa wanda yace hakan barazanane ga ci gaban Najeriya.
Yace yanda ake shirin mayar da mulkin Najeriya babu ‘yan adawa abin damuwa ne musamman yanda ‘yan adawar ke komawa jam’iyya me mulki saboda abinda zasu samu ba dan kishin masa ba.
Yace hakan baranane ga Dimokradiyyar Najeriya.
Yace idan aka bar abubuwa suka ci gaba da lalace wa hakan ba karamar illanzai wa Najeriya da al’ummarta ba.
Ya bayyana hakane a ganawar da aka yi dashi a kafar BBCHausa.