Friday, December 5
Shadow

Wadannan dakikan Gwamnonin naku da suka bayar da hutun makaranta saboda zuwan watan Ramadan ‘ya’yansu basa zuwa wadannan makarantun gwamnatin, sun kai ‘ya’yansu can makarantun kudi a Abuja ko kasashen waje>>Omoyele Sowore ya gayawa ‘yan Arewa

Tsohon dan takarar shugaban kasa, kuma mawallafin jaridar Sahara Reporters, Omoyele Sowore ya bayyana cewa, Jahilan Gwamnonin da suka bayar da hutun makaranta saboda zuwan watan Ramadan ‘ya’yansu basa zuwa wadannan makarantun Gwamnatin da suka kulle.

Ya kara da cewa, sun kai ‘ya’yansu can makarantun kudi a Abuja ko kuma kasashen waje.

Sowore ya bayyana hakane a shafinsa na sada zumuntar Facebook.

A baya ma dai Sowore ya kira Gwamnonin jihohin Kebbi, da Kano, da Bauchi da Katsina da cewa Jahilaine saboda sun kulle makarantu saboda zuwan watan Ramadan.

Inda yace idan ya zama shugaban kasa, ba zai yadda a rika kulle makarantun ba.

Karanta Wannan  Kalli Subhanallahi Ana ta yada Bidiyon kirkira na AI dake nuna wai shugaba Buhari yayi mummunan karshe, Saidai mutane nata Allah wadai da fadar cewa hukuncin bawa na ga mahaliccinsa

Lamarin kulle makarantun dai ya jawo cece-kuce sosai inda cikin wadanda suka soki hakan hadda kungiyar Kiristoci ta CAN, da Ministar Ilimi, Suwaiba Ahmad.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *