Friday, April 10
Shadow

Wanda ya gayamin nine zanci zabe a 2023 ya sake gayamin nine zan ci zaben 2027>>Inji Shugaba Tinubu

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa an gaya masa shine zai ci zaben shekarar 2027.

Ya bayyana hakane a yayin da ya je addu’ar 7 ta marigayin basaraken jihar Ogun, Awujale, Oba Sikiru Adetona.

Shugaba Tinubu yace a yayin da yake yakin neman zaben shugaban kasa a 2022, ya kaiwa basaraken ziyara inda ya saka masa albarka sannan ya gaya mai cewa shine zai yi nasara a zaben.

Sannan yace ya kuma kara gaya mai cewa shine dai zai sake lashe zaben shekarar 2027.

Shugaba Tinubu yace amma yanzu gashi ya tafi ya barmu a Duniya.

Karanta Wannan  Mutane Miliyan 1.9 ne suka nemi aikin Fire Service, Immigration, da Civil Defence da aka bude kwanannan, yayin da mutane dubu 30 ne kadai za'a dauka, Kalli Yawan mutanen da suka nema daga kowace jiha

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *