Tuesday, May 27
Shadow

‘Yar Shekaru 16 ta yi Gàrkùwà da kanta inda ta nemi iyayenta su biya kudin fansa Naira Miliyan 2

Matashiya ‘yar kimanin shekaru 16 wadda ke ajin SS2 a makarantar Sakandare ta yi garkuwa da kanta inda ta nemi a biya kudin fansa Naira Miliyan 2.

Lamarin ya faru ne a Abakaliki, Jihar Ebonyi.

Matashiyar ta kira dan uwanta inda ta sanar dashi cewa an yi garkuwa da ita.

Wani dake da alaka da iyayenta ne ya taimaka mata wajan shirya wannan lamarin.

Kakakin ‘Yansandan jihar, Joshua Ukandu ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace an kama wadanda ake zargi kuma sa’a tabbatar an hukuntasu.

Karanta Wannan  Dan Gwamnan Jihar Neja, Marwan Bago Ya Zama Babban Matukin Jirgin Sama Na Kamfanin Jirage Na 'Overland Airways', Inda Har Ya Yi Sawu Daya Zuwa Abuja

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *