Saturday, January 10
Shadow

Yarbawa sunce basu yadda da kotunan shari’ar musulunci a jihohinsu ba

Kungiyoyin dake fafutukar kafa kasar Yarbawa sun bayyana rashin amincewa da bullar kotunan shari’ar Musulunci a jihohinsu.

Jihar Ekiti itace ta baya-bayannan da aka samu bullar kotun shari’ar Musulunci wadda har alkalai 3 Imam Abdullahi Abdul-Mutolib, Imam Abdulraheem Junaid-Bamigbola da Dr. Ibrahim Aminullahi-Ogunrinde sun yi zama sun saurari shari’ar rikicin aure guda biyu.

Kamin nan a jihohin Lagos, Ogun, Oyo and Osun ma an samu ,aman kotun shari’ar Musuluncin.

Zuwa yanzu, Jihar Ondo ce kadai bata da kotun shari’ar Musulunci a cikinta, hakanan itama Gwamnatin jihar Ekiti ta musanta cewa akwai kotun shari’ar musulunci a cikinta.

Tuni dai aka samu wani Fasto me suna Pastor Oluwafemi J. Edafemi, ya jagoranci gamayyar wasu masu ruwa da tsaki a yankin na Yarbawa inda suka yi gangamin cewa basu yadda da kotunan shari’ar Musulunci a jihohin nasu ba.

Karanta Wannan  Ni na fara yin takarar Musulmi da Musulmi na ci zabe, kuma Tinubu ma yayi ya ci zabe, idan wani ya isa ya gwada yin Kirista da Kirisa muga ko zai kai labari>>El-Rufai

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *