Tuesday, February 3
Shadow

Zamu doke APC da PDP a 2027, Kwankwaso ne zai zama shugaban kasa>>Inji Jam’iyyar NNPP

Jam’iyyar NNPP ta bayyana cewa a zaben shekarar 2027 zata doke Jam’iyyun APC da PDP.

Shugaban Jam’iyyar, Dr. Ajuki Ahmad ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a Abuja inda yace zasu yi nasarar hakanne ta hanyar jagoransu, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso wanda shine zai zama shugaban kasar Najeriya a 2027

Duk da rikicin cikin gida da ya mamaye Jam’iyyar ta NNPP, Dr. Ajuki Ahmad yace a yanzu sun samu zaman lafiya a cikin Jam’iyyar.

Yace duk da yake hakan ba abune me sauki ba amma sun sha Alwashin cimma burinsu inda yace zasu fitar da Najeriya daga halin data tsinci kanta a ciki.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo wani gida a Kano inda me gidan ke baiwa Samari dakuna haya ta dan awanni lokaci suka kai 'yan matansu suna Aikata Alfasha, itama tana bada kanta da 'ya'yanta mata

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *