Thursday, February 5
Shadow

Zuwa yanzu, Shugaba Tinubu ya shafe kwanaki 181 a kasashen waje tun bayan hawansa mulki

Jam’iyyar ADC ta caccaki shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu saboda yawan tafiye-tafiyen da yake yi zuwa kasashen waje.

Jam’iyyar ta bayyana hakane ta bakin kakakinta, Bola Abdullahi inda yace ana kashe kudaden Talakawa wajan tafiye-tafiyen shugaban kasar.

Ya bayyana cewa, wannan shine karo 40 da shugaba Tinubu zai bar Najeriya tun bayan hawansa mulki kuma ya kwashe kwanaki 181 a kasashen waje.

Sanarwar tace wannan kusan watanni 6 kenan da shugaba Tinubu ya kwashe a kasashen wajan.

ADC tace tana Allah wadai da irin wadannan tafiye-tafiyen na shugaban kasa musamman ganin cewa babu wani abin ci gaba da hakan ya kawowa kasarnan.

Karanta Wannan  Sau 35 kenan nake zuwa aikin Umrah, na biya kudin Jirgi Naira Dubu 1>>Inji Wannan Hajiyar

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *