Saturday, March 15
Shadow

An kama magidanci da Abokinsa da sukawa Agolarsa fyàdè, suka dirka mata ciki

Mahukunta a jihar Legas sun kama magidanci dan kimanin shekaru 38 da abokinsa da suka hadu sukawa agolarsa me shekaru 14 fyade.

Kakakin ‘yansandan jihar, CSP Benjamin Hundeyin ya tabbatar da faruwar hakan a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a ranar Asabar.

Ya kara da cewa, mahaifiyar yarinyarce ta kai koke a ofishin ‘yansanda dake yankin Okokomaiko na jihar.

Rahoton yace sun dirkawa yarinyar ciki inda a yanzu tana dauke da cikin wata 9.

Ya kara da cewa, da zarar an kammala bincike, za’a gurfanar da wanda ake zargin a kotu.

Karanta Wannan  Da Duminsa: Matatar Man fetur din Dangote ta rage farashin man

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *