Saturday, March 15
Shadow

Ya kamata a binciki Sanata Akpabio kan zargin làlàtà da Natasha Akpoti tai masa>>Inji Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar yayi kira ga shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da shugabancin majalisar dattijai da cewa ya kamata au binciki kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio kan zargin da Sanata Natasha Akpoti tai masa na son yin lalata da ita.

Atiku a sanarwar da ya fitar ya nemi cewa a matsayin Akpabio na mutum na 3 wanda yafi karfin fada aji a Najeriya, ya kamata ace yana da mutunci da tsare kai da tarbiyya.

Atiku yace ya kamata a kafa kwamiti na musamman me zaman kansa da zai binciki sanata Akpabio kan wannan zargi.

Atiku yace wannan lamari zai sa Duniya ta fahimci irin tsarin Adalci da Najeriya ke da shi.

Karanta Wannan  An kama mutane 3 a jihar Naija saboda baiwa me ciki Naira Miliyan 30 dan ta yadda su cire cikinta me watanni 6 dan yin tsafi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *