Friday, December 5
Shadow

Najeriya ce kasa ta 3 da ta fi yawan bashi a Afrika

Bankin (Afreximbank) ya bayyana cewa, Najeriya ce kasa ta 3 a jerin kasashen da suka fi yawan cin bashi a Africa.

A wani bayani da ya fitar, bankin yace yawan ciyo bashi daga kasashen waje a tsakanin kasashen Adrica na ci gaba da karuwa.

Yace hakan na faruwane saboda rashin ci gaban bangaren hada-hadar kudi na kasashen Afrikan.

Bankin yace a watanni 6 na farkon shekarar 2024, kasashen Afrika 10 ne ke da kaso 69 na yawan bashin da aka ciwo a nahiyar.

Kasashen sune South Africa (14%), Egypt (13%), Nigeria (8%), Morocco (6%), Mozambique (6%), Angola (5%), Kenya (4%), Ghana (4%), Côte d’Ivoire (3%), sai Senegal (3%).

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon Tauraron Fina-finan Hausa, Musa Mai Sana'a tare da tare da wani dan kasar waje yana masa Turanci amma Musan ya kasa bayar da amsa da kyau, wasu dai sun ce bai iya bane inda wasu ke cewa da gangan yayi

Bankin yace hakan na kara karuwane saboda yawan dogaron da kasashen ke yi da samun kudi ta hanyar neman tallafi daga kasashen yamma.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *