Saturday, March 15
Shadow

Gwamnatin Sokoto ta ƙaddamar da tallafin azumi ga masu buƙata ta musamman

Gwamnatin jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin Najeriya ta ƙaddamar ta tallafin azumi ga masu buƙata ta musamman a faɗin jihar.

Cikin wata sanarwa da gwamnatin jihar ta ftitar, ta ce tallafin – wanda ya ƙunshi rabon kuɗi – zai shafi masu buƙata ta musamman duka ƙananan hukumomin jihar.

Yayin da yake jawabi a wajen ƙaddamarwar gwamnan jihar, Ahmad Aliyu ya ce tallafin zai shafi cibiyoyi 27 na masu buƙata ta musamman a fadin jihar.

Gwamnan kuma yi kira ga waɗanda za su amfana da tallafin su bayar da haɗin kai domin kauce wa turmutsitsi a wajen raba tallafin

Karanta Wannan  Zamu kawo man fetur da ya fi na Dangote sauki daga kasashen waje>>Inji 'Yan kasuwar Man fetur na Najeriya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *