
Asusun bayar da lamuni na duniya, IMF, ya roƙi gwamnatin Najeriya da ta fito da wasu hanyoyin samar wa al’umma yadda za su rage tasirin raɗaɗin da suke ji sakamakon matakan da ta ɗauka domin inganta tattalin arzki.
A cewar IMF duk da matakin da gwamnatin ta ɗauka na cire tallafin man fetur ya zama wajibi, amma kuma ya haifar da wahalhalun rayuwa ga ƴan Najeriya da dama.
Bankin lamunin ya ce a yanzu tsananin talauci a ƙasar ya ƙaru ya zuwa kashi 47 a cikin shekarar 2024 da ta gabata.