Wednesday, March 19
Shadow

Me magana da yawun shugaban kasa ya nemi a zartar da hukuncin ķķìsà kan matashiya ‘yar bautar kasa data soki Gwammatin Tinubu

Rahotanni sun bayyana cewa, me taimakawa shugaban kasa kan yada labarai, Temitope Ajayi ya nemi a zartar da hukuncin kisa kan matashiya Ushie Uguamaye saboda sukar da tawa shugaba Bola Ahmad Tinubu.

Kafar peoplesgazette ce ta wallafa cewa Temitope Ajayi ya nemi a yankewa Ushie hukuncin kisa saboda yace a zartar mata hukunci mafi tsanani da hukumar bautar kasa ta NYSC ta tanadar.

Saidai a bayaninsa, Ajayi, ya bayyana cewa, shi ba haka yake nufi ba, an canja masa manufar bayaninsa ne dan cimma wani buri.

Yace abinda yake nufi da zartarwa da Ushie hukunci mafi tsanani a dokar NYSC shine a koreta daga aikin bautar kasar, yace shi a iya saninsa wannan ne hukunci mafi tsanani a dokar NYSC ba hukuncin kisa ba.

Karanta Wannan  'Yan kasuwar Man fetur da yawa basa sayen man fetur din daga matatar mu>>Dangote

Lamarin Ushie ya dauki hankula sosai inda ciki hadda Atiku Abubakar, da Peter Obi da kungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty international sun saka baki a ciki.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *