Thursday, March 20
Shadow

Majalisar mu ta dattijai kamar kungiyar tsafi take, kowane Sanata na tsoron ya soki kakakin majalisa, Akpabio ya taba rike min hannu ya rika murzawa, kowace mace akawa haka tasan abinda ake nufi>>Sanata Natasha Akpoti ta sake yiwa Akpabio tonon silili

Har yanzu dai Sanata Natasha Akpoti bata saurara ba da yiwa kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio tonon silili.

A sabuwar hirar da ta yi da BBC Pidgin, Natasha tace majalisarsu kamar kungiyar tsafi take.

Tace kowane sanata na tsoron ya bayyana ra’ayin da ya sha banban da na kakakin majalisar saboda tsoron kada a saka masa ido.

Tace amma zargin da takewa Sanata Godswill Akpabio da gaskene, ta sake maimaita cewa akwai sanda suka je gidansa ya kama hannunta a gaban mijinta ya ja ya suna tafiya, tace ya rika murza mata hannu, tace kowace mace akawa haka tasan abinda ake nufi.

Karanta Wannan  Innalillahi Wa'inna Ilaihi Raji'un: Gobara a gidan babban Sakataren (Perm. Sec.) na ma'aikatar Matasa da wasanni ta jahar Sokoto Muhammad Bello Yusuf tayi sanadiyyar rasuwar matarsa da 'ya'ya 3 da mai aiki ɗaya

Tace hakanan akwai sanda ta manta ta tafi aiki da sauri bata dauki zoben alkawarinta na aure ba, tace Sanata Godswill Akpabio na ganinta sai yake ce mata yaya Natasha, naga baki saka zoben aurenki ba, mu shigo ne, tace a gaban kusan sanatoci 5 ne hakan ta faru.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *