Tuesday, February 3
Shadow

Tsohuwar Ministar Jin Kai, Betta Edu da aka sauke saboda zargin karkatar da kudin Talakawa ta samu kyautar girmamawa a jami’ar Calabar

Tsohuwar minister Jin kai, Betta Edu wadda aka sauke saboda zargin karkatar da kudaden talakawa ta bayyana a wajan bikin cika shekaru 50 da kafuwar jami’ar Calabar dake jihar Cross-River.

Wani abin mamaki shine har kyautar karramawa aka baiwa ministar.

Da yawa sun yi mamakin ganin Ministar a bainar jama’a tana ta sha’aninta.

Kyautar da aka bata itace ta tallafawa al’umma da ta yi.

Daga cikin zarge-zargen kudaden da akawa ministar a baya sun hada da na Naira Miliyan N585 da kuma na Dala $640,000.

A baya dai tsohuwar ministar ta kuma shiryawa Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero shan ruwa a gidanta.

Karanta Wannan  A Karshe Dai Mutumin Da Ya Yi Tattaki Daga Jigawa Zuwa Kano Domin Ganin Gwamna Abba Kabir Ya Isa Kofar Fadar Gwamnatin Kano, Inda Ya Ce Ko Zai Yi Shekara Guda Ba Zai Tafi Ba Har Sai Ya Ga Abba

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *